NewsHausa NewsHausa

Pages

LATEST POSTS

Friday, 31 August 2018

Kalli Yadda Wasu Wasu Barayi Sukama Wata DPO Tsirara A Kasuwa

A wata hira da tayi da manema labarai, wata DPO din 'yan sanda a Abuja ta bayyana yanda wasu 'yan daba suka wahalar da ita, yayin da suka je kama kayan sata a wata kasuwa dake Abuja.

A wata hira da tayi da manema wata DPO din 'yan sanda a Abuja ta bayyana yanda wasu 'yan daba suka wahalar da ita, yayin da suka je kama kayan sata a wata kasuwa dake Abuja. CSP Nana Bature Garba tace sai da aka gargade ta akan cewar kar ta sake ta shiga kasuwar Panteka dake unguwar Mpape a birnin Abuja, saboda irin hadarin da ke cikin kasuwar.

Ga dai irin bayanin da ta yiwa manema labarai. "Sunana CSP Nana Bature Garba. Ina so na bayyana muku labarin abinda ya faru dani lokacin da na ke DPO Mpape. Lokacin dana je Mpape suna da wata ka'ida cewa baka isa ka shiga kasuwar Panteka ka kama wani ba, ko ka dauki kayan mutane da aka sace a wajen.

Ni kuma sai nace ya za'ayi a ce 'yan sanda na wuri ace ba za'a shiga wurin ba, ni kam sai na shiga. Na tara 'yan sanda nace mu je. Ko kafin muje wurin ma mutanen Mpape suka dinga zuwa suna gargadina akan kada mu shiga wurin.

Abinda nake tunani shine, kamar akwai masu kai musu rahoto, domin kuwa ina kyautata zaton, kamar sun samu labarin muna zuwa. Domin kuwa muna zuwa wurin suka zagaye mu, suka sakar mana karnuka, muna budewa karnukan wuta, kamar daman abinda suke jira kenan, suka dinga jifan mu da duwatsu da sanduna ta ko ina a jikin mu.

A cikin 'yan sanda mu 18 da muka je wurin babu wanda bai ji ciwo ba. Sai da suka yi mana dukan tsiya, domin ko ni kaina da nake DPO sai da suka yaga min kayana suka yi mini tsirara, sai wata mata ce ta zo ta bani zani na daura. Sannan muka yi waya aka kawo mana agaji, kafin 'yan agajin su zo mun riga mun galabaita, ko tashi bama iya yi.

Da Allah ya bani lafiya, na ce ni kuwa wannan wurin ko menene a ciki sai na sani, na ce sai na sake komawa, saboda haka sai na rubutawa kwamishinana, na ce ina so a taimake ni mu samu a zo mu sake shiga wannan wurin, muga abinda za'a iya yi.

Sai ya ce to, tun daga wannan lokacin muka buda hanya, muke samu muna shiga wannan wuri, duk wanda aka yiwa sata zamu je wurin ayi bincike a kama wanda yake da laifi." Wannan shine takaitaccen labari na da gwagwarmayar dana sha a kasuwar Panteka dake Mpape Abuja.

Kalli Hoton Mawaki Davido Ya Fara NYSC a Lagos

Shahararren mawakin nan, David Adeleke Adedeji wanda ake kira da Davido yana ci gaba da jan hankalin ma'abota shafukan sada zumunta a Najeriya bayan da ya fara aikin yi wa kasa hidima wato NYSC a ranar Laraba.

Mawakin ya shiga sansanin masu yi wa kasa hidimar na unguwar Iyana Ipaja a jihar Legas.

Wajibi ne dai kowane dan Najeriya wanda bai wuce shekara 30 da haihuwa ya yi aikin yi wa kasa hidimar bayan kammala digiri da babbar difloma.

Davido ya rika wallafa hotunansa sanye da kakin 'yan yi wa kasa hidimar.

Wasu hotunan da aka ringa watsawa a shafukan sada zumunta sun nana mawakin wanda shahararren attajiri ne, tare da masu yi wa kasa hidima sun yanyame shi.

Ace singer and celebrity, Adeleke David Adedeji (DAVIDO), LA/18B/6389 as he registered for 2018 Batch 'B' Stream 2 Orientation Course at the Lagos NYSC Camp,Iyana Ipaja,Agege.

Posted by NYSC LAGOS on Tuesday, 28 August 2018

Wednesday, 29 August 2018

Kalli Yanda Kunama Ta Maqale Jikin Wandon Wani Mutumi

A rika duba kaya kamin a saka

Wannan hoton na fadakarwa ne akan a yi hankali da saka kayan da suka jima a jiye ba tare da dubawaba, kamar yanda ake iya gani a hoton, ga kunama nan tayi lamo a jikin wandon inda ace da tsautsai ya saka, saidai aji wani labarin daban.

Shafin Sarauniyane ya wallafa hoton wannan wando da kiran mutane akan a rika lura.

Manyan sarakunan Najeriya guda 4 da ba su da aure

Manyan sarakunan Najeriya guda 4 da ba su da aure
Sanannen abu ne a kusan kowanni kabila ko addini cewa aure muhimmin abu ne, kuma ita cikar kamalar mutum mace ko namiji, hakan ta sanya aure ya fi zama cancanta ga shuwagabanni, don haka zaka ga da zarar wani ya samu mukami sai yayi aure, ba duka aka zama daya ba, inda a Najeriya aka samu wasu manyan sarakuna dake mulkin manyan masarautu amma basu da aure, ku biyo mu.

Wadannan sarakunan basu da aure har yanzu, duk da suna gudanar da mulkin dubunnan al’umma.

Sarkin Gombe

Sarkin Gombe, mai martaba Alhaji Abubakar Shehu na Uku ya dane mukamin Sarki kuma shugaban majalisar sarakunan jihar Gombe ne yana shekaru 39 bayan mutuwar mahafinsa, Alhaji Sheu Abubakar kimanin shekaru uku da suka shude.

Sai dai duk da cewa a yanzu haka yana da shekaru 42, amma Sarki Abubakar bai taba aure ba, kuma bashi da mata a ko ina, a duk fadin jihar Gombe da ma Najeriya gaba daya, wanda hakan na damun al’ummar jihar Gombe.

Majiyoyi sahihai sun tabbatar da cewar a yayin da za’a nada shi sarautar Sarkin Gombe, an so a daura masa guda daga cikin yayan Sarkin Musulmi amma abin bai yiwu ba, haka zalika aurensa da diyar Sarkin Dukku, Gimbiya Aisha Musnan saura kiris, amma abin bai yiwu ba.

Amma duk da wannan nakasu, Sarki Abubakar yana da kyakkyawar alaka da jama’ansa, talakawansa na kaunarsa sakamakon taimakon dayake musu.

Sarkin Ife (Ooni Ife)

Sarkin Ife na daga cikin matasan sarakuna a Najeriya, kuma shine shugaban majalisar sarakunan jihar Osun gaba daya, yayi aure har sau biyu, amma auren bai dade ba, aurensa na karshe a ranar 12 ga watan Maris na shekarar 2016 aka yi, inda ya auri Sarauniya Wuraola Zaynab Otiti Obanor, amma suka rabu a shekarar 2018.

Tun bayan wannan mutuwar aure wanda hatta sadakin daya biya saida aka dawo masa dasu, Ooni mai shekaru 43 bai sake wani auren ba, sai dai ana samun jita jitan cewa ya kusa angwancewa, inda ake danganta shi da Sarauniyar Kyau Tobi Philips.

Sarkin Agbor (Dein Agbor)

Dein na Agbor, Sarkin masarautar Agbor dake jihar Delta, Benjamin Ikechukwu Kiagborekuzi I shine wanda ya zama Sarki tun yana karamin yaro dan shekara 2, 1979 bayan rasuwar mahafinsa, a yanzu yana da shekaru 42 amma shima har yanzu bashi da mata.

Dayake Benjamin ya dade a kasar waje yana karatu, don haka tun bayan dawowarsa Najeriya a shekarar 2001 ake zargin wai buduwarsa baturiya zai aura, amma mambobib majalisarsa sun ce atabau ba zai auri baturiya ba, yar kabilar Agbor zai aura.

Sai dai shima Basaraken yana da girma sosai a idon jama’ansa, suna matukar kaunarsa tare da mutunta shi.

Sarkin Ubulu-Uku (Obi Ubulu-Uku)

Sarkin al’ummar Ubulu Uku dake jihar Delta, Oba Chukwuka Akaeze I ya dare karagar mulki ne a shekarar 2016 yana dan shekara 15 bayan miyagu masu garkuwa da mutane sun kashe mahaifinsa Edward Ofulue III, ma’ana yanzu shekararsa 17, inda ya kwashe shekaru biyu yana mulkar jama’a amma bashi da aure.

Amma a iya cewa karancin shekaru ne suka hana Oba Akaeze aure, don kuwa a yanzu haka yana kasar waje yana karatu, kamar yadda jaridar Aminiya ta ruwaito.
Naij.com

Labari me matukar ban mamaki: Shekaru 4 bayan aure sunata jima'ai amma har yanzu matar na nan da budurcinta


Duniyarnan sai mutum yayi tunanin ya gama jin abin mamaki sai wani sabo ya fito, wani labarine daya fito daga kasar China ke bayyana wasu ma'aurata da sukayi aure sama da shekaru 4 amma matar tana nan a sabuwar budurwarta saboda sunata yin jima'ai ba ta daidaiba a rashin sani, damuwar rashin haihuwa da suka shiga ciki ce ta sa labarin ya bayyana.

Ma'auratan wanda ba'a bayyana sunayensu ba saidai shekaru, matar tana da shekaru 24 mijin kuwa yana da shekaru 26, kamar yanda kafar watsa labarai ta Mirror ta kasar Ingila ta ruwaito.

Sunje asibiti sukawa likita korafin cewa suna ta jima'ai akai-akai tun bayan aurensu, yanzu shekaru 4 kenan amma babu maganar daukar ciki. Likitar da suka samu me suna Liu Hongmei ta bayyana cewa ma'auratan matasane kuma suna da lafiya dan haka abin da ban mamaki.

Matar ta mata korafin cewa tana jin zafi sosai lokacin jima'in amma saboda son haihuwa take jurewa.

Likita Liu ta bayyana cewa, ta sa a bincika matar sai suka gano wani abu me matukar ban mamaki, abinda suka gano kuwa shine matar haryanzu budurcinta na nan kamar budurwar da bata san namiji ba.

Da bincike yayi tsanani sai aka gano ashe ta dubura suke jima'ai shiyasa bata dauki ciki ba.

Bayan gano hakane, likita Liu ta zaunar da ma'auratan ta musu hudubar yanda ake jima'ai sannan ta basu littafin dake koya ilimin jima'i.

Da take hira da manema labarai, likitar tace, abin mamakine kuma ba'a cika samun irin wannan lamari ba ace ma'aurata sunyi aure tsawon shekara 4 amma basu san yanda ake daukar ciki ba.

Bayan 'yan watanni kadan sai ga ma'auratan sun dawo da kyautar kwai 100 da kaza ga asibitin saboda matar ta dauki ciki.

Kalli Hoton Hadiza Gabon daya birge

Hoton Hadiza Gabon daya birge

Tauraruwar fina-finan Hausa, Hadiza Gabon kenan a wannan hoton nata da ya kayatar, tasha kyau, tubarkallah, muna mata fatan Alheri.

Kalli Zafafan Hotunan Jaruma FATI WASHA


Tauraruwar fina-finan Hausa, Fati Washa kenan a wadannan kayatattun hotunan nata da tasha kyau, tubarkallah,muna mata fatan Alheri.