Kasar Lebanon ta dauke 'yan mata sanye da gajerun wanduna aikin 'yansanda dan jan hakalin turawa - NewsHausa NewsHausa: Kasar Lebanon ta dauke 'yan mata sanye da gajerun wanduna aikin 'yansanda dan jan hakalin turawa

Pages

LATEST POSTS

Sunday 24 June 2018

Kasar Lebanon ta dauke 'yan mata sanye da gajerun wanduna aikin 'yansanda dan jan hakalin turawa

Kasar Lebanon ta dauke 'yan mata sanye da gajerun wanduna aikin 'yansanda dan jan hakalin turawa

Kasar Lebanon ta fara baiwa 'yan sanda 'yan mata gajerun wanduna dan su rika jawo hankulan turawa masu yawon bude ido kasar, magajin garin Baroummana inda abin ya faru me suna pierre Achkar ya bayyan cewa wanan tsari da suka fito dashi sunyi ne dan canja tunanin kasashen yamma akan kasar.

Lamarin dai ya Jawo cece-kuce tsakanin 'yan kasar amma wasu na ganin cewa hakan ba komai bane.

Wani dan kasuwa da kafar watsa labarai ta Reuters tayi hira dashi yace yana da shago a bakin kasuwa kuma 'yan matan 'yansandan na tsayuwa a bakin shagon nashi suna aiki, shi bega aibun wannan abinba, ya kara da cewa duka matan sun san abinda suke, sun kuma kammala jami'a dan haka ba zasu yarda su yi abinda be dace ba.

Itama wata ma'ikaciyar 'yarsandan da aka yi hira da ita tace ba a tilasta mata yin aikin ba da kanta ta nema kuma tana jin dadin aikin.

Copy the link below and Share with your Friends:

Download Our Official Android App on Google Playstore HERE
OR
Download from another source HERE



No comments:

Post a Comment