Labari Mai Dadi A Kannywood : Auren Sadiya Kabala Yazo - NewsHausa NewsHausa: Labari Mai Dadi A Kannywood : Auren Sadiya Kabala Yazo

Pages

LATEST POSTS

Wednesday 11 April 2018

Labari Mai Dadi A Kannywood : Auren Sadiya Kabala Yazo

A RANAR Asabar ɗin wannan makon, wato 14 ga Afrilu, 2018, za a ɗaura auren ɗaya daga cikin jarumai mata da ke Kaduna, wato Sadiya Kabala.
Za a ɗaura auren ta da sahibin ta mai suna a masallacin Juma'a na Al-Mannar da ke Kaduna da misalin ƙarfe 1:00 na rana.

A jerin tsarin bikin wanda mujallar Fim ta gani, an nuna cewa za a fara shagalin auren a ranar Alhamis ɗin nan a lambun shaƙatawa na Ƙofar Gamji.
Bayan ɗaurin auren kuma za a yi dina a wani otal mai suna Silver Sand da ke Titin Katuru, Unguwar Sarkin Musulmi.
To Allah ya sa a ce gara da aka yi, amin.

Copy the link below and Share with your Friends:

Download Our Official Android App on Google Playstore HERE
OR
Download from another source HERE



No comments:

Post a Comment