MALAMIN ISLAMIYARMU BA SHI DA TAJWIDI, YA WAJABA MU CANZA SHI ?    - NewsHausa NewsHausa: MALAMIN ISLAMIYARMU BA SHI DA TAJWIDI, YA WAJABA MU CANZA SHI ?   

Pages

LATEST POSTS

Saturday 13 August 2016

MALAMIN ISLAMIYARMU BA SHI DA TAJWIDI, YA WAJABA MU CANZA SHI ?   

MALAMIN ISLAMIYARMU BA SHI DA TAJWIDI, YA WAJABA MU CANZA SHI ?                                     
Tambaya:

Malam tambaya ta itá ce mun bude islamiya ta matar aure, to malamin da yake karantar da qur'an yana da matsalan tajweed kuma ya ki bar ma wani ya karantar Dan Allah Dr munada laifi cikin kuràkuran da yake koyarwa ?

Amsa:

Allah ya yi umarni da karanta Alqur'ani  kamar yadda ya saukar, kamar yadda aya ta hudu a suratul Muzzamil ta yi nuni zuwa hakan.                                                                                                      
wasu malaman musuluncin suna kasa tajwiidy gida biyu, akwai na dole kamar fitar da harufa kamar yadda suke a larabci, akwai na mustahabbi kamar yawancin maddoji.                                                   
Fitar da harufa wajibi ne saboda yana iya canza fassarar Alqur'ani.                         

Akwai wasu bangarorin na tajwidi wadan da ba wajibi ba ne dabbaka su, saboda Annabi (s.a.w) ya tabbatar da lada biyu ga wanda yake dagarawa a karatun Alqur'ani, kamar yadda ya zo a hadisin Muslim.                                                 

Allah ne mafi Sani

Amsawa: Dr Jamilu Zarewa.
9/8/2016.



Copy the link below and Share with your Friends:

Download Our Official Android App on Google Playstore HERE
OR
Download from another source HERE



No comments:

Post a Comment