HUKUNCIN MIKEWA MALAMI KO SHUGABA SABODA GIRMAMAWA|DR JAMILU YUSUF ZAREWA - NewsHausa NewsHausa: HUKUNCIN MIKEWA MALAMI KO SHUGABA SABODA GIRMAMAWA|DR JAMILU YUSUF ZAREWA

Pages

LATEST POSTS

Tuesday 29 November 2016

HUKUNCIN MIKEWA MALAMI KO SHUGABA SABODA GIRMAMAWA|DR JAMILU YUSUF ZAREWA

HUKUNCIN MIKEWA MALAMI KO SHUGABA SABODA GIRMAMAWA



Tambaya:
Mal. Ina tp ne yanzu, kuma idan na je aji yara suna mikewa damin gaishe ni mal. na barsu su cigaba ko na dakatar da su ?


Amsa :
To dan'uwa akwai malaman da suka ta fi akan cewa makaruhi ne a mikewa malami, akwai wadanda kuma suka halatta. Saidai maganar da ta fi ita ce bai hallata malami ya nemi a mike masa ba, saboda fadin Annabi s.a.w. " Duk wanda ya so mutane su mike masa to ya tanaji wurin zamansa a wuta" 

kamar yadda tirmizi ya rawaito shi kuma ya kyautata shi a hadisi mai lamba ta : 2755, Albani kuma ya inganta shi a silsilatussahih
ah lamba ta : 5957 Amma idan aka mikewa mutum ba tare da ya nema ba, to wannan babu laifi ga wanda ya mike da wanda aka mike saboda shi, domin ya zo a hadisi cewa : 


Annabi s.a.w. ya mikewa zaid bn haritha lokacin da ya dawo daga tafiya, kamar yadda ya zo a hadisin da tirmizi ya rawaito shi kuma ya kyautata shi a lamba ta : 2732,

saidai wasu malaman sun raunana wannan hadisin kamar albani a dha'ifuttirmizi 1\326

Allah ma fi sani

Amsawa
Dr jamilu zarewa


Copy the link below and Share with your Friends:

Download Our Official Android App on Google Playstore HERE
OR
Download from another source HERE



No comments:

Post a Comment