Gwamnati Ta Yi Gargadi Kan Matsayin Askarawan ' Peace Corps' - NewsHausa NewsHausa: Gwamnati Ta Yi Gargadi Kan Matsayin Askarawan ' Peace Corps'

Pages

LATEST POSTS

Tuesday 19 September 2017

Gwamnati Ta Yi Gargadi Kan Matsayin Askarawan ' Peace Corps'


Ministan Kasafin kudi ya gargadi al'ummar Nijeriya musamman matasa kan cewa Shugaba Buhari bai karbi wani kudiri daga majalisar tarayya ba kan Askarawan 'Peace Corps' ballantana a fara yayata cewa Shugaban kasa kadai ake jira ya rattaba hannu kan kudirin don ya zaman doka ta yaddd za a bude kafa na daukar aikin Askarawan.

Ya ce har yanzu kudirin yana gaban majalisar tarayya don haka ya gargadi matasa kan su yi takatsantsa don ganin ba a yaudare su ta hanyar sayar masu da fom inda ya yi nuni da cewa gwamnati ta samu labarin cewa a wasu jihohi har an yi nisa wajen mallakar kakin Askarawan da zimmar cewa za a kaddamar da shirin nan ba da jimawa ba.

Copy the link below and Share with your Friends:

Download Our Official Android App on Google Playstore HERE
OR
Download from another source HERE



No comments:

Post a Comment