Ta Baro Jamhuriyyar Nijar Zuwa Nijeriya Don Ta Yi Ido Hudu Da Mawaki Umar M. Sharif - NewsHausa NewsHausa: Ta Baro Jamhuriyyar Nijar Zuwa Nijeriya Don Ta Yi Ido Hudu Da Mawaki Umar M. Sharif

Pages

LATEST POSTS

Monday 29 January 2018

Ta Baro Jamhuriyyar Nijar Zuwa Nijeriya Don Ta Yi Ido Hudu Da Mawaki Umar M. Sharif


Daga Umar Ridwan

Wannan yarinyar da kuke gani sunanta Maryam. Ta niko gari tun daga Niger zuwa Nijeriya don ta ga shaharren mawakin finafinan Hausan nan dake jihar Kaduna, wato UMAR M SHARIF wanda ta ce yana bala'in burge ta shi ya sa ta keso mafarkinta na yin ido hudu da shi ya zamo gaskiya.

'Yar shekara 17 da haihuwa, Maryam ta ce suna zaune ne a Maradi. Ta kara da cewa iyayenta sun rabu kuma tana yawace-yawace wanda ke sa mahaifiyarta cewa yawon karuwanci ta keyi, abunda a cewarta ke ba ta mata rai, shi ya sa ta taho Kaduna a don ta yi waka da gogan nata Umar M Sharif ko za ta ji sanyi a ranta. Yau kimanin kwanta 2 kenan a Kaduna. 

Idan Allah ya sa akwai wanda ya san Umar M Sharif ya sanar da shi cewa wata masoyiyar shi na neman shi. Za mu saka cikakkiyar hirar gobe a cikin shirin GARI YA WAYE a tashar DITV/Alheri Radio Kaduna. Ku saka ido!

Copy the link below and Share with your Friends:

Download Our Official Android App on Google Playstore HERE
OR
Download from another source HERE



No comments:

Post a Comment