Taƙaitacen Tarihin Jarumar kannywood Halima Atete - NewsHausa NewsHausa: Taƙaitacen Tarihin Jarumar kannywood Halima Atete

Pages

LATEST POSTS

Saturday 16 September 2017

Taƙaitacen Tarihin Jarumar kannywood Halima Atete



Halima Atete ta dade da fara harkara fina-finan Hausa, amma ba tayi suna sosai ba Yar asalin Jihar Borno ce. Tauraruwar kan fito a matsayin wata muguwa a wasa kusan a ko yaushe.

Halima Yusuf Atete ba fim kadai ba tayi karatun law har zuwa matakin Diploma, ta fara karatun ta ne da fari a Garin Maiganari daga nan kuma ta koma wata Makarantar Gwamnati da ke Yerwa.

Daga baya ma ta koma Kwalejin nan ta Mohammed Goni inda tayi difiloma a shari’a.

Kamar yadda ta bada labari, tace tana ganin su Ali Nuhu da wani Directer wanda abokin yayanta ne Ahmed A Bifa sunzo Gidansu daukar fim, sai taji tana sha'awar shiga harkar,
To bayan ta samu kudinta shine ta taho KANO wajen wata babarta, zuwa wani lokaci sai dai aka ganta a fim wanda babanta yaso ya hana amma daga baya ya hakura ya kyaleta.

Halima ta fito a fina-finai irin su Kona Gari, Asalina, Dakin Amarya, Hannu da Hannu, Maza Da Mata dss. tayi fina-finai sun kai 150.

Ta kai an taba bata kyauta na ‘Yar wasar da ta fi kowa a cikin shekarun nan.
Atete tana taimakawa wadanda rikicin Boko Haram ya shafa a Garin su.

Yanzu haka kuma ta kafa wata Gidauniya Domin taimakawa kananan yara.

Halima yar Real Madrid ce ta mutuwa yanzu haka kuma tana Makkah domin yin aikin Hajji.

Copy the link below and Share with your Friends:

Download Our Official Android App on Google Playstore HERE
OR
Download from another source HERE



No comments:

Post a Comment