News: Amurka za ta fallasa Iran - NewsHausa NewsHausa: News: Amurka za ta fallasa Iran

Pages

LATEST POSTS

Sunday 4 February 2018

News: Amurka za ta fallasa Iran

Amurka za ta fallasa Iran

Amurka ta ce za ta gabatar da gyauron makamai waɗanda ta ce Iran ce ta samar wa ƴan-tawayen Huthi na Yemen.

Jakadiyar Amurka a majalisar ɗinkin duniya Nikkey Haley za ta nuna shaidar ga wakilan ƙasashen kwamitin sulhu na majalisar dinkin duniya, a ƙoƙarin da Amurka ke yi na ganin majalisar ɗinkin duniya ta ƙara takura wa Iran.

Watanni da dama ke nan tun bayan da ƙasar ta Amurka ke bibiyar majalisar ɗinkin duniya wajen ganin ta hukunta Iran, inda har Amurka ɗin ta yi barazanar ficewa daga yarjejeniyar jingine shirin makamin nukila da aka ƙulla da Iran.

Tuni dai Iran ta musanta cewa tana samar wa ƴan-tawayen Huthi makamai, sannan ta bayyana shirin Amurka ɗin a matsayin na bogi.

Copy the link below and Share with your Friends:

Download Our Official Android App on Google Playstore HERE
OR
Download from another source HERE



No comments:

Post a Comment