Yadda Anka Kaddamar Da Taron Gabatar Da Fim Din Sarauniya - NewsHausa NewsHausa: Yadda Anka Kaddamar Da Taron Gabatar Da Fim Din Sarauniya

Pages

LATEST POSTS

Saturday 2 December 2017

Yadda Anka Kaddamar Da Taron Gabatar Da Fim Din Sarauniya



Daga Wakilinmu, Kano
Kamfanin shirya finafinai na Rite Time Multimedia ya shirya wani taron biki na gabatar a fim din Sarauniya da ya kammala aikin wanda a ke sa ran na gaba kadan za a shigar da shi kasuwa.

Taron wanda a ka gudanar a ranar Asabar 25 ga watan Nuwamba a babban dakin taro na otel din Ni’ima da ke cikin garin Kano, an fara shi ne da misalign karfe 8 na dare. Tun da farko da yake jawabi a game da wanan aro, Muhammad Mujahid ya bayyana manufar taron ne da nufin za a haska wani bangare na wannan fim ne Sarauniya domin jama’a su gani daga wani bangare da fim din ya kunsa, sannan kuma za a bayar da kyautittika na karamawa ga jaruman da suka bada gudunmuwa a cikin wannan fim din.

Don haka a ka gayyato manyan mutane su gani don su san irin aikin da wannan kamfni na Rite Time yake gudanarwa. Domin kuwa kamfani ne da ya dade yana kawo ci gaba a masana’antar mu ta Kannywod wajen shirya finafinai masu inganci da samawa matasa usu da aikin yi. Don haka muna fatan Allah ya sa nasara a wannan taro, Allah ya sa mu yi lafiya mu tashi lafiya.”
Bayan gama jawabi ne sai aka gabatar da ‘yan rawar koroso inda suka dauki lokaci suna nishadantar da taron.



Copy the link below and Share with your Friends:

Download Our Official Android App on Google Playstore HERE
OR
Download from another source HERE



No comments:

Post a Comment