Wasika Zuwa Ga Matasa - Daga Sheikh Aminu Ibrahim Daurawa - NewsHausa NewsHausa: Wasika Zuwa Ga Matasa - Daga Sheikh Aminu Ibrahim Daurawa

Pages

LATEST POSTS

Monday 26 March 2018

Wasika Zuwa Ga Matasa - Daga Sheikh Aminu Ibrahim Daurawa

Babban malamin addini Sheikh Aminu Ibrahim Daurawa yayi wasika zuwa ga matasa na wannan kasar nigeriya da su yi amfani da wannan damar ta samartaka kafin ta gushe musu. 

Shehin mallamin yayi wannan wasika ne ga matasa 'ya'yan talakawa akan yadda suke rayuwa a cikin wannan kasar ga jawabinsa. 

"BAYAN GAISUWA DA FATAN ALKHAIRI,
INA YI MUKU ADDU'A DA FATAN SHIRIYA
WASU SUNA KIRANKU YAN JAGALIYA, 
WASU SUNA KIRANKU YAN SARA SUKA, 
 WASU SUNA KIRANKU YAN SHARA, 
 WASU SUNA KIRANKU YAN DABA, 
 WASU SUNA KIRAN SU YAN KALARE,
AMMA NI INA KARANKU MATASA MASU DARAJA , DA WASU MARASA KISHI SUKE AMFANI DA KU, DOMIN BIYAN BUKATUN SU NA SIYASA
A LOKACIN DA YAYANSU SUNA MANYAN MAKARANTU, DA MANYAN GIDAJE DA MAKUDAN KUDADE,
KUN TABA GANIN DAN WANI YANA SAI BABANSA
KIN TABA GANIN MATAR WANI DAGA CIKIN SU A WANNAN HALI DA SUKA JEFA KU.?
DON ALLAH KU YI WATSI DA WANNAN RAYUWAR KU KAMA ILMI DA SANAA.
MUYI TIR DA ALLAH WADAI GA MASU BATA MANA RAYUWAR MATASA".

Copy the link below and Share with your Friends:

Download Our Official Android App on Google Playstore HERE
OR
Download from another source HERE



No comments:

Post a Comment