An kai wadda ake zargi da kashe mijinta Maryma Sanda gidan yari a Abuja - NewsHausa NewsHausa: An kai wadda ake zargi da kashe mijinta Maryma Sanda gidan yari a Abuja

Pages

LATEST POSTS

Friday 24 November 2017

An kai wadda ake zargi da kashe mijinta Maryma Sanda gidan yari a Abuja

Matar da ake zargi da kashe mijinta, Maryam Sanda, ta bayyana a gaban wata babbar kotu da ke Abuja ranar Juma'a.

bayan ta daba masa kwalba a sassan jikinsa

Al'amarin ya faru ne a gidan ma'auratan da ke unguwar Wuse a Abuja.
Lauya mai shigar da kara ya ce suna so su sauya tuhume-tuhume saboda sabbin hujjoji da aka samu sakamakon bincken da ake yi mata.
Maryam ta shiga kotun ne tana rungume da jaririyarta da kuma Al-Kur'ani a hannunta, inda ta lullube fuskarta ba a iya gani.

Ana tuhumurta da daba wa mijinta fasasshiyar kwalba a kirji wanda ya yi sanadin mutuwarsa, amma ta musanta hakan tana mai zubar da hawaye.
Tuhuma ta biyu an ce ta ji masa ciwo da kwalba a kirji wanda ya yi sanadin mutuwarsa, a nan ma Maryam ba ta amsa yin laifin ba.

Lauya mai kare wadda ake kara ya ce ba sa sukar dage zaman shari'ar sai dai suna so a ba da wadda ake zargi beli.

Kotun dai ta bayar da umarni a atsare ta a gidan yari na Suleja.
Daga nan ne Alkalin Kotun Yusuf Halilu ya dage zaman shari'ar zuwa ranar 7 ga watan Disamba.

Copy the link below and Share with your Friends:

Download Our Official Android App on Google Playstore HERE
OR
Download from another source HERE



No comments:

Post a Comment